(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

1. Halitta

Image

Ga yadda farkon kome ya faru. Allah ne ya halicce duniya da dukan kome a cikin kwana shida. Bayan da Allah ya halicce duniya, ta cika da duhu da wofi, amma Ruhun Allah yana shawagi bisa ruwaye.

Image

Allah ya ce, "Bari haske ya kasance!," sai kuwa ya kasance. Allah ya ga hasken yana da kyau sai ya kira shi yini. Ya raba shi da duhu, wanda ya kira dare. Allah ya halitta haske a rana ta fari ta halitta.

Image

A rana ta biyu ta halitta, Allah ya yi Magana ya halicci sama da ƙasa. Ya yi sama ta wurin raba ruwayen sama da ruwayen ƙasa.

Image

A rana ta uku, Allah ya yi Magana sai ya raba ruwaye da bushashiyar ƙasa. Ya kirayi bushashiyar ƙasar, duniya, ruwayen kuma teku. Allah ya gani yana da kyau.

Image

Sai Allah ya ce, "Bari ƙasa ta fid da tsire-tsire na masu bada tsaba, da itatuwa masu bada ƴaƴa, kowane bisa ga nasa iri." Allah ya gani yana da kyau.

Image

A rana ta huɗu ta halitta, Allah ya yi Magana sai ya halicce rana, da wata, da tauraru. Allah ya halicce su don su bada haske ga duniya, su raba yini da dare, lokacin shekara. Allah ya gani yana da kyau.

Image

A rana ta biyar, Allah ya yi Magana sai ya halicce da kowane irin mai rai cikin ruwaye da duk tsuntsaye. Allah ya gani yana da kyau, sai ya albarkace su.

Image

A rana ta shida Allah ya ce, "Bari dabbobi iri-iri su kasance a duniya!" Ya kasance kamar yadda Allah ya faɗa. Waɗansu dabbobin gona, waɗansu dabbobi masu rarrafe, waɗansu dabbobin daji. Sai Allah ya ga yana da kyau.

Image

Sai Allah ya ce, "Bari mu yi mutum cikin siffarmu, da kamanninmu. Shi yi mulkin duniya da dukan dabbobi."

Image

To Allah ya ɗauki laka, ya siffanta mutum, sai ya hura masa rai. Sunan mutumen Adamu. Allah ya kafa gona inda Adamu zai zauna, sai ya sa ya kula da ita.

Image

A tsakiyar gonar, Allah ya shuka irin itace biyu: icce na rai da icce sanin nagarta da mugunta. Allah ya cewa Adamu yana iya cin ƴaƴan kowane icce cikin gona amma banda ƴaƴa na iccen sanin nagarta da mugunta. Idan ya kuwa ci shi zai mutu.

Image

Sai Allah ya ce, "Bai kyautu ba mutum ya kasance shi kaɗai." Amma ba dabbobin da suke iya zama mataimakan Adamu.

Image

Sai Allah ya sa Adamu barci mai yauni. Sai Allah ya ɗauki daga haƙarƙarinsa ya halitta mace, ya kuwa kawo mashi ita.

Image

Da Adamu ya gan ta, sai ya ce, "Wannan tana kama da ni! Bari mu kira ta mace, gama an halicce ta daga namiji." Domin haka mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa ya kuwa zama ɗaya da matarsa.

Image

Allah ya halicce mutum da mace cikin kamanninsa. Ya albarkace su ya kuma ce masu, "Ku hayayyafa ƴaƴa, ku cika duniya!" Sai Allah ya ga duk abin da ya halitta yana da kyau sosai, ya ƙayatas da shi. Dukan wannan ya faru a cikin rana ta shida ta halitta.

Image

Da rana ta bakwai ta yi, Allah ya gama aikinsa. Sai Allah ya huta da duk abin da ya yi. Ya albarkaci rana ta bakwai, ya tsarkake ta domin a wannan rana ne ya huta daga aikinsa. Haka ne Allah ya halitta duniya da duk abin da ke cikinta.

Labarin LMT daga Farawa 1-2