(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

28. Mai Arziki, Saurayi Mai Mulki

Image

Wata rana, wani mai arziki, saurayi mai mulki, ya zo wurin Yesu, kuma ya tambaye shi, "Malam managarci, me zan yi in sami rai na har abada?" Yesu ya ce masa, "Me ya sa kake kirana 'managarci' ? Allah kaɗai ne 'managarci'. Amma in kana so ka samu rai madawami, yi biyayya da dokokin Allah."

Image

"Waɗanne zan yi biyayya da su?" ya tambaya. Yesu ya amsa, "Kada ka yi kisan kai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi ƙarya. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka."

Image

Amma saurayin ya ce, "Na kiyaye dukan waɗannan dokoki tun ina yaro. Me kuma zan ƙara yi domin in rayu har abada?" Yesu ya dube shi, kuma ya ƙaunace shi.

Image

Yesu ya amsa, "In kana so ka zama cikakke, je ka saidan dukan mallakarka, kuma ka ba matalauta kuɗin. Za ka samu ajiya a sama. Kuma sai ka zo ka bi ni."

Image

Da saurayin ya ji abin da Yesu ya ce, sai ya cika da baƙin ciki domin yana da arziki sosai, kuma ba ya so ya rabu da duk mallakarsa. Sai ya juya baya, ya bar Yesu.

Image

Sai Yesu ya fadawa almajiransa, "Zai yi wuya ga mutane masu arziki su shiga mulkin Allah! Haka ne, ya fi sauki ga raƙumi ya bi ta ƙofar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah."

Image

Da almajiran suka ji maganar Yesu, sun razana, kuma suka ce, "Ke nan wa yake iya tsira?"

Image

Yesu ya dubi almajiran, kuma ya ce, "Ga mutane ba abu mai yiyuwa ba ne, amma ga Allah, kome ya yiyuwa."

Image

Bitrus ya cewa Yesu, "Mun bar kome mun bika. Mene ne ladanmu?"

Image

Yesu ya amsa, "Duk wanda ya bar gidajensa, ƴanuwansa maza, ƴanuwansa mata, mahaifinsa, mahaifiyarsa, ƴaƴansa, ko mallakarsa domina, zai samu sakamako kashi 100 fiye da haka nan, kuma zai samu rai madawami. Amma da yawa na fari za su zama na ƙarshe, kuma da yawa na ƙarshe za su zama na fari."

Labarin LMT daga Matiyu 19:16-30; Marƙus 10:17-31; Luka 18:18-30