(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

23. Haifuwar Yesu

Image

Maryamu tana tare da wani mutum mai sanin gaskiya, mai suna Yusufu wanda yake tashenta. Da ya sami labari Maryamu tana da ciki, ya sani cewa ba ɗansa ba ne. Ba ya so ya sa Maryamu kunya, sai ya tsara ya rabu da ita a ɓoye. Kafin ya yi haka nan, wani mala'ika ya yi magana da shi a mafalki.

Image

Mala'ikan ya ce, "Yusufu, kada ka ji tsoro ka ɗauki Maryamu kamar matarka. Ɗan da yake cikinta daga Ruhu Mai Tsarki ne. Za ta haifi ɗa. Raɗa masa suna Yesu (ma'ana, 'Yahweh yana ceto'), domin zai ceci mutane daga zunubensu."

Image

Sai Yusufu ya auri Maryamu, kuma ya tafi da ita gida kamar matarsa, amma ba ya kwana da ita ba har sai da ta haifu.

Image

Da lokaci ya yi da Maryamu za ta haifu, Kaisar Augustus, sarkin sarakuna Daular Roma, ya umurci dukan jama'a su je a rubuta su a garin inda kakaninsu suka zauna. Yusufu da Maryamu sun yi tafiya mai nisa daga inda suke a Nazarat zuwa Baitalami sabili da kakansu Dauda ya fito daga Baitalami.

Image

Da suka iso Baitalami, babu wurin zama. Ɗakin kaɗai da suke iya samu sai a cikin makiyaya inda dabbobi suke zama. An haifi ɗan a can, kuma uwarsa ta sa shi cikin tsummoki don ba su da gado dominshi. Suka sa mashi suna Yesu.

Image

Wannan daren akwai makiyaya a gonakin kusa suna gadin gargunansu. Ba zato ba tsammani sai mala'ika mai haske ya bayana garesu, sai suka ji tsoro. Mala'ikan ya ce, "Kada ku ji tsoro domin ina da labari mai daɗi dominku. Almasihu, Mai iko, an haife shi a Baitalami!"

Image

"Ku je ku nemi jaririn, za ku same shi a nannaɗe a cikin tsummoki yana kwance a makiyaya." Ba zato ba tsammani sai samai suka cika da mala'iku masu yabon Allah, suna cewa, "Ɗaukaka ga Allah a cikin sama, kuma salama a duniya ga mutanen da ya fi ƙauna!"

Image

Makiyayan sai suka zo nan da nan a wurin da Yesu yake, kuma sai suka ganshi kwance a makiyaya kamar yadda mala'ikan ya faɗa. Sun cika da murna. Makiyaya sun koma cikin gonakai inda tumakinsu suke, can suna raira waƙoƙin yabo ga Allah domin duka abin da suka ji da kuma suka gani.

Image

Bayan ɗan wani lokaci, shehuna daga ƙasashe masu nisa na gabas, suka ga wani sabon tauraro a sama. Sai suka gane da cewa wani sabon sarkin Yahudawa ya zo duniya. Sai suka yi tafiya mai nisa don sun ziyarci wannan sarkin. Sun zo Baitalami, kuma sun sami wurin da Yesu da iyayensa suke zama.

Image

Da shuhunan suka ga Yesu tare ta uwarsa, suka rusuna ƙasa, suka yi masa sujada. Sun baiwa Yesu kyautai masu tsada. Sai suka koma gida.

Labarin LMT daga Matiyu 1; Luka 2