(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

36. Ɗaukakar

Image

Wata rana, Yesu ya ɗauki uku daga cikin almajiransa, Bitrus, Yakubu da Yahaya tare da shi. (Almajirin mai sunan Yahaya ba shine ba Yahaya mai baftisma.) Suka tafi sama bisan dutsi don su keɓe su yi addu'a.

Image

Sa'adda Yesu yake addu'a, fuskarsa ta zama da haske kamar rana, kuma tufafinsa suka zama farare kamar haske, farare fiye da kowane a duniya yake iyawa.

Image

Sai Musa da annabi Iliya suka bayyana gareshi. Waɗannan mutane sun rayu a duniya shekaru ɗaruruwa da suka wuce. Sun yi magana da Yesu a kan mutuwarsa, da za ta faru ba da daɗewa ba a Urshalima.

Image

Yayin da Musa da Iliya suke magana da Yesu, Bitrus ya ce wa Yesu, "Yana da kyau mu kasance a nan. Bari mu yi runfa uku, ɗaya dominka, ɗaya don Musa, kuma ɗaya domin Iliya." Bitrus bai san abin da yake cewa ba.

Image

Sa'ad da Bitrus yake magana, hadiri mai hasken gaske ya sauko ya kewaye su, kuma murya daga sama ta ce, "Wannan ɗana ne ƙaunatace. Ina farin ciki da shi. Ku saurare ni." Almajiran uku suka firgita, suka faɗi a ƙasa.

Image

Sai Yesu ya taɓa su ya ce, "Kada ku ji tsoro. Ku tashi." Da suka duba kewaye da su, babu kowa sai Yesu kaɗai.

Image

Yesu da almajiran uku suka koma gida daga dutsen. Sai Yesu ya ce masu, "Kada ku faɗawa kowa abin da ya faru a nan tukuna. Zan mutu ba da daɗewa ba, kuma zan komo rayayye. Bayan wannan, kuna iya faɗawa mutane."

Labarin LMT daga Matiyu 17:1-9; Marƙus 9:2-8; Luka 9:28-36