(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

11. Idin Ƙetarewa

Image

Allah ya faɗakar da Fir'auna da in ya ci gaba da ƙin yarda Isra'ilwa su tafi, to zai kashe dukan ƴaƴan fari na mutanen Masar da na dabbobi. Da Fir'auna ya ji haka nan ya ƙi ya gaskanta ko ya yi biyayya ga Allah.

Image

Allah ya tanada hanya ceton ƴaƴan farin na duk waɗanda suka gaskanta da shi. Kowane iyali za ya zaɓi ɗan rago maras aibi ya kashe shi.

Image

Allah ya faɗa wa Isra'ilawa su shafa jinin ɗan ragon a jikin kofar gidansu, su kuma gasa naman su cinye shi da sauri, tare da gurasa maras yis (yisti). Ya kuma faɗa masu su fita daga Masar bayan sun ƙare ci.

Image

Isra'ilawa sun yi daidai yadda Allah ya umurce su. A tsakiyar dare, Allah ya sauko, ya kashe dukan ƴaƴan fari na Masar.

Image

Dukan gidajen Isra'ilawa a shafe suke da jini kewaye da ƙofarsu, sai Allah ya ƙetare gidajen nasu. Dukan wanda yake ciki ya tsira. An cece su saboda jinin ɗan rago.

Image

Amma Masarawa ba su gaskanta ko su yi biyayya ga Allah ba. Sai Allah ya bi bisan gidajensu. Allah ya kashe duka ɗan fari na Masarawa.

Image

Dukan ɗan fari namiji na Masar ya mutu, daga ɗan fari na cikin kurkuku, zuwa ɗan farin Fir'auna. Mutane da yawa cikin Masar suka yi ta kuka mai tsannani sabili da baƙin cikinsu.

Image

A wannan daren, Fir'auna ya kira Musa da Haruna ya ce, "Ɗauki Isra'ilawa ku fita daga Masar yanzu-yanzu!" Masarawa kuma suka matsawa Isra'ilawa su bar ƙasar nan da nan.

Labarin LMT daga Fitowa 11:1-12:32