(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

16. Masu Ƙuɓutar

Image

Bayan da Joshuwa ya mutu, Isra'ilawa suka yi wa Allah rashin biyayya, kuma basu kori sauran Kan'aniyawa da suke a ƙasar ba. Sai Isra'ilawa suka fara bauta wa allolin Kan'aniyawa maimakon Yahweh, Allah na gaskiya. Isra'ilawa ba su da sarki a lokacin nan, ke nan kowa yana yin abin da ya dama.

Image

Sabili da Isra'ilawa sun ci gaba da take dokokin Allah, ya hore su ta wurin barin ƴaƴan gaba su ci nasara a kansu. Wannan ƴaƴan gaban suka sace abubuwan Isra'ilawa, suka hallaka gidajensu, suka kashe da yawa daga cikinsu. Bayan shekaru da dama na tawaye ga Allah da kuma zama a ƙalƙashin ƴaƴan gaba, Isra'ilawa sun tuba, kuma suka roƙi Allah ya cece su.

Image

Sai Allah ya tanada masu mai fansa wanda ya cece su daga ƴaƴan gabansu, ya kuma kawo salama cikin ƙasar. Amma mutanen suka manta da Allah hallo, kuma sai suka shiga bautar gumaka. Sai Allah ya sa Madayanawa, kabila ƴaƴan gaba a kusansu, suka ci su da yaƙi.

Image

Madiniyawan suka ɗauki dukan girbin Isra'ilawa na shekara bakwai. Isra'ilawan sun tsorota sarai har suka ɓuya cikin kogon duwatsu inda Madiniyawan ba za su same su ba. A ƙarshe sai suka yi ƙara ga Allah don ya cece su.

Image

Wata rana, wani mutumen Isra'ila mai suna Gidiyon yana susukar alkama daga ɓoye don kada Madayanawa su sace mashi. Mala'ikan Yahweh ya zo gun Gidiyon ya ce, "Allah na tare da kai, babban jarumi. Je ka ka ceci Isra'ila daga Madayanawa."

Image

Baban Gidiyon yana da bagadi domin gumki. Allah ya faɗa wa Gidiyon ya rushe wannan bagadin. Amma Gidiyon yana jin tsoron mutane, sai ya bari dare ya yi. Sai ya rushe bagadin, ya kuma ragolgwaje shi. Ya sake gina sabon bagadi na Allah kusan na gumkin, ya miƙa hadaya ga Allah bisanshi.

Image

Da safiya ta waye mutane suka ga wani ya rushe, ya hallaka bagadin, sai suka husata sarai. Sai suka je gidan Gidiyon don su kashe shi, amma baban Gidiyon ya ce, "Me ya sa ku ke ƙoƙari ku taimaki allahnku? In shi allah ne ya ceci kansa mana! Domin ya faɗi wannan, mutanen basu kashe Gidiyon ba.

Image

Sai Madayanawa suka komo su yi wa Isra'ilawa sata. Su da yawa ne har sun fi gaban ƙirge. Gidiyon ya kira Isra'ilawa tare don su yaƙe su. Gidiyon ya roƙi Allah ya gwada masa alamu biyu don ya tabbata da cewa lalle Allah zai yi anfani da shi ya ceci Isra'ila.

Image

Domin alama ta fari, Gidiyon ya shinfiɗa zane a ƙasa, kuma ya roƙi Allah ya bar raɓar safe ta rufe zanen ƙaɗai, kada ta rufe ƙasa. Allah ya yi haka. Dare mai zuwa, ya yi roƙo ƙasar ta jiƙe amma banda zanen. Allah ya yi haka kuma. Waɗannan alamu biyu sun sa Gidiyon ya yarda da cewa Allah zai yi anfani da shi ya ceci Isra'ila daga Madayanawa.

Image

Sojojin Isra'ilawa 32,000 suka zo gun Gidiyon, amma Allah ya shaida masa sun yi yawa. Sai Gidiyon ya kori 22,000 da suke jin tsoron yaƙi. Allah ya kuwa cewa Gidiyon sun dai yi yawa har yanzu. Sai Gidiyon ya ƙara korar su sai sauran sojoji 300.

Image

Da dare, Allah ya cewa Gidiyon, "Sabka cikin zangon Madayanawa, idan ka ji abin da suke cewa, ba za ƙara jin tsoro ba." Sai wannan daren, Gidiyon ya sabka zangon, kuma ya ji abin da wani sojin Madayanawa yake gayawa abokinsa a kan mafalkinsa. Abokin mutumen ya ce, "Wannan mafalkin yana nufin sojojin Gidiyon za su ci Madayanawa da yaƙi!" Da Gidiyon ya ji wannan, sai ya yabi Allah.

Image

Sai Gidiyon ya koma wurin sojojinsa ya baiwa kowanensu ƙafo, da tulun laka, da jiniya. Sai suka kewaye sansanin inda sojoji Madayanawa suke barci. Mutanen Gidiyon 300 ɗin suna riƙe da jiniyoyin a cikin tulun don Madayanawa kar su ga hasken jiniyoyin.

Image

Sai dukan sojojin Gidiyon suka kashe tulunan nasu gami guda, nan da nan sai hasken wutar jiniyar ya tashi. Suka busa ƙahoni, suka yi ƙara, "Takobi don Yahweh kuma don Gidiyon!"

Image

Allah ya rikita Madayanawa, sai suka fara faɗa ma junansu, kuma suka kashe kansu. Nan da nan sauran Isra'ilawa aka kira su daga gidajensu, su zo su taimaka a kori Madayanawa. Suka kashe da yawa daga cikinsu, kuma suka kori sauran waje da ƙasar Isra'ilawa. Madayanawa 120,000 suka mutu wannan rana. Allah ya ceci Isra'ila.

Image

Mutanen suka so su naɗa Gidiyon sarkinsu. Gidiyon bai yardar masu haka nan ba, amma ya tambaye su zoben zinariya da kowanen su ya ɗauke daga Madayanawa. Mutanen suka ba Gidiyon zinariya da yawa.

Image

Gidiyon ya yi anfani da zinariya ya ɗumka keɓeɓɓen sutura kamar na babban firist. Amma mutanen suka fara yi masa sujada kamar gumki. Sai Allah ya sake hukunta Isra'ila domin bautar gumaka. Allah ya bar ƴaƴan gabansu su ci su da yaƙi. Sai suka roƙi taimakon Allah, kuma Allah ya aike masu da wani mai fansa.

Image

Wannan hali ya faru sau da yawa: Isra'ilawa su yi zunubi, Allah ya hore su, su tuba, kuma Allah sai ya aike masu mai fansa ya cece su. Shekaru da yawa Allah ya aike da masu fansa don ceton Isra'ilawa daga abokan gabansu.

Image

A ƙarshe, mutanen sun roƙi Allah ya ba su sarki kamar sauran al'ummai. Suna bikatar sarki mai tsawo, kuma mai ƙarfi, wanda yake iya jagorancin su ciki yaƙi. Allah bai ji daɗin wannan roƙo ba, amma ya ba su sarkin kamar yadda suka tambaya.

Labarin LMT daga Alkalawa 1-3; 6-8