(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

47. Bulus da Silas a Filibi

Image

Da Shawulu yake tafiya cikin Daular Roma, ya fara anfani da sunan shi na Roma, "Bulus." Wata rana, Bulus da abokinsa Silas suka tafi wani garin Filibi su shaida bisharar Yesu. Suka tafi wani wuri kusan kogi waje da garin inda mutane suka taru su yi addu'a. Can suka sadu da wata mace da ake kira Lidiya mai kasuwanci. Tana kauna kuma tana yabo Allah.

Image

Allah ya bude zuciyar Lidiya ta bada gaskiya da sako a kan Yesu, kuma ita da iyalinta aka yi masu baftisma. Ta gayaci Bulus da Silas su zauna a gidanta, sai suka zauna da ita da iyalinta.

Image

Bulus da Silas suka sadu da mutane a wurin addu'a. Kowace rana yayin da suke tafiya can, wata yarinya baiwa, mai aljani ta bi bayan su. Ta wurin wannan aljani tana wa mutane duba, ta samu kuɗi da yawa don uwayen gidanta.

Image

Baiwar ta ci gaba da kiransu da karfi sa'ad da suke tafiya, "Wadannan mutane ma'aikatan Allah Maɗaukaki ne. Suna faɗa maku yadda za ku tsira!" Ta yi haka nan so da yawa har Bulus ya damu.

Image

A karshe, wata rana da baiwar ta fara kara, Bulus ya juya gareta ya ce wa aljanin da ke cikinta, "A cikin sunan Yesu fita daga cikinta." Nan take aljanin ya fita.

Image

Mutumen mai baiwar ya husata sarai! Sun gane da cewa banda aljanin, baiwar ba za ta iya duba ba. Ke nan mutane ba za su kara biyan kuɗi ga uwayen gidanta, domin ta yi musu duba.

Image

Sai uwayen gidan baiwar suka kai Bulus da Silas wurin hukumar Roma inda aka buge su, kuma aka sa su cikin kurkuku.

Image

Sai suka sa Bulus da Silas cikin wuri mafi tsarare cikin kason, kuma suka ɗaure kafafunsu da sarƙoƙi. Kuma cikin tsakiyar dare suka ci gaba suna raira waƙoƙin yabo ga Allah.

Image

Ba zato ba tsammani, sai aka yi girgizar ƙasa! Dukan ƙofofin kurkuku suka buɗe, kuma sarƙoƙin dukan ƴan kason suka zube.

Image

Mai gadin kurkukun ya tashi, da ya ga ƙofofin kaso a buɗe, ya tsorota! Ya yi tsammani dukan ƴan kaso sun gudu, sai ya nufa ya kashe kanshi. (Ya sani hukumar Roma za su kashe shi in ya bar ƴan kaso sun tsere). Amma Bulus ya gane shi, kuma ya kira shi, "Tsaya! Kada ka ji wa kanka ciwo. Duka muna nan."

Image

Mai gadin ya yi rawar jiki da yake isa wajen Bulus da Silas, ya tambaya:" Me zan yi in samu ceto?" Bulus ya amsa:" Gaskanta ga Yesu Ubangiji, kuma kai da iyalinka za ku tsira". Sai mai gadin ya kai Bulus da Silas cikin gidansa, kuma ya wanke ciwonsu. Bulus ya shaida bisharar Yesu ga kowa cikin,

Image

Mai gadin kason da duk iyalinsa suka bada gaskiya kuma aka yi masu baftisma. Sai mai gadin ya baiwa Bulus da Silas abinci, kuma suka yi murna tare.

Image

Ranar gobe shugabanni garin suka saki Bulus da Silas daga kurkuku, kuma suka ce masu su bar Filibi. Bulus da Silas suka ziyarci Lidiya da sauran abokansu, kuma suka bar garin. Labari mai daɗi a kan Yesu ya ci gaba da yaduwa, kuma Ekklisiya ta ci gaba da girma.

Image

Bulus da sauran shugabannin krista suka yi tafiya zuwa garuruwa da yawa, suna shaida bishara, kuma suna koyas da mutane a kan Yesu. Suka kuwa rubuta wasiƙoƙi da yawa na ƙarfafawa da na koyaswa masu bi cikin Ekklisiyoyi. Wasu daga waɗannan wasiƙoƙi suka zama littatafai Littafi Mai Tsarki.

Labarin LMT daga Ayyukan Manzanni 16: 11-40