(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

45. Istifanas da Filibus

Image

Ɗaya daga cikin shugabannin Ekklisiyar farko, wani mutum ne da ake kira Istifanas. Yana da halin kirki, kuma yana cike da Ruhu Mai Tsarki. Istifanas ya yi al'ajabai da yawa, kuma ya yi shelar gaskiya da mutane ya kamata su gaskanta da Yesu.

Image

Wata rana, sa'ad da Istifanas yake koyaswa a kan Yesu, wasu Yahudawa da ba su yarda ba da Yesu suka fara jayayya da Istifanas. Sai suka husata ƙware, kuma suka yi ƙarya a kan Istifanas ga shugabannai addinai. Suka ce, "Mun ji shi yana saɓo akan Allah da Musa!" Sai shugabannin addinai suka kama Istifanas, suka kai shi wurin babban firist da sauran shugabannin Yahudawa, inda shaidun ƙarya da yawa suka yi ƙarya a kan Istifanas.

Image

Babban firist ya tambayi Istifanas, "Waɗannan abubuwan gaskiya ne?" Istifanas ya amsa masu ta tuna masu da manyan abubuwan da Allah ya yi tun daga lokacin Ibrahim har zuwa lokacin Yesu, kuma ƙaƙa mutanen Allah suka ta yi masa rashin biyyaya. Sai ya ce, "Ku taurarrun mutane ƴan tawaye kun yas da Ruhu Mai Tsarki koyaushe, kamar yadda kakannunku koyaushe suka yas da Allah, kuma suka kashe annabawansa. Amma kun yi mugunta fiye da hakanan! Kun kashe Almasihu!"

Image

Da shugabannin addini suka ji haka, sun husata sosai har suka rufe kunnuwansu, kuma suka yi ƙara da ƙarfi. Suka kai Istifanas bayan gari, kuma suka jefa masa duwatsu don su kashe shi.

Image

Da Istifanas yake mutuwa, ya yi ƙara ya ce,"Yesu karɓi ruhuna." Sai ya faɗi a gwiwawunsa ya yi ƙara kuma, "Malam, kada ka ɗaura masu wannan laifi." Sai ya mutu.

Image

Wani saurayi mai sunan Shawulu ya yarda da mutanen da suka kashe Istifanas, kuma suka riƙe rigunansu yayin da suke jifansa da duwatsu. Wannan rana, mutane da dama a Urshalima suka fara tsanantawa masu bin Yesu. Sai masu bin suka ƙaura zuwa wasu wurare. Amma duk da wannan suka ci gaba da bisharar Yesu ko'ina suka je.

Image

Wani almajirin Yesu mai sunan Filibus yana ɗaya daga cikin masu bi da suka tsere daga Urshalima lokacin tsanani. Ya tafi Samariya inda ya yi bisharar Yesu, kuma mutane da yawa suka tsira. Sai wata rana, wani mala'ikan Allah ya cewa Filibus ya je kan wata hanya cikin hamada. Da yake tafiya kan hanya, Filibus ya ga wani babban ma'aikacin hukuma na Habasha yana tafiya cikin keken dokinsa. Ruhu Mai Tsarki ya cewa Filibus ya je ya yi magana da mutumen.

Image

Da Filibus ya kusato keken dokin, ya ji Bahabashen yana karatu daga abin da annabi Ishaya ya rubuta. Mutumen ya karanta, "Suka kai shi kamar ɗan rago a kashe shi, kuma ɗan rago ya yi shuru, bai ce komi ba. Suka wulaƙanta shi, kuma ba su darajanta shi ba. Suka ɗauke masa ransa."

Image

Filibus ya tambayi Bahabashen, "Ko kana gane abin da kake karantawa? Bahabashen ya amsa,"A'a. Ban iya in gane ba in ba wani ya bayyana mini. In ka yarda zo ka zauna kusana. Ishaya yana rubutu a kanshi ne ko a kan wani ne?"

Image

Filibus ya bayyana wa Bahabashen Ishaya yana rubutu a kan Yesu. Filibus kuma ya yi anfani da sauran littatafai ya faɗa masu bisharar Yesu.

Image

Da Filibus da Bahabashen suka yi tafiya, sai suka iso wurin wani ruwa. Bahabashen ya ce,"Duba! Akwai wani ɗan ruwa! Ana iya mini baftisma?" Sai ya cewa mai tuƙin ya tsaida keken dokin.

Image

Sai suka sauka cikin ruwan, kuma Filibus ya yi wa Bahabashen baftisma. Da suka fito daga cikin ruwan, Ruhu Mai Tsarki, nan da nan ya kai Filibus wani wuri inda ya ci gaba da faɗawa mutane labarin Yesu.

Image

Bahabashen ya yi tafiyarsa zuwa gidansa, yana murna da ya san Yesu.

Labarin LMT daga Ayyukan Manzanni 6:8-8:5; 8:26-40