(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

33. Labarin Mai Shuka

Image

Wata rana, Yesu yana koyar da babban taro kusan gefen wani tafki. Mutane da yawa suka zo su saurare shi, sai Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa a bakin tafkin don ya samu wuri isashe ya yi magana da su. Ya zauna a cikin jirgin ruwan, kuma ya koyas da mutanen.

Image

Yesu ya faɗi wannan labarin, "Wani mai shuka ya tafi waje ya shuka iri. Yayin da yake watsa irin da hannunsa, waɗansu suka faɗa a kan hanya, sai tsuntsaye suka zo suka cinye dukan irin.

Image

"Waɗansu suka faɗa kan ƙasa mai dutse, babu ƙasa mai nisa. Irin cikin ƙasa mai duwatsu ya tsiro nan da nan, amma jijiyoyin ba su iya zuwa nesa ba cikin ƙasar. Da rana ta fito, kuma wokaci ya yi zafi, subkar ta bushe, kuma ta mutu."

Image

"Haka nan wasu iri suka faɗa cikin ƙayoyi. Shukar ta fara girma, amma ƙayoyin suka shaƙe su. Sai shukar daga cikin ƙayoyin ba su iya bada ƴaƴa ba.

Image

"Wasu iri suka faɗa cikin ƙasa mai kyau. Waɗannan suka fito, kuma suka bada ƴaƴa kashi 30, 60 har ma 100 hiye da waɗanda aka shuka. Bari mai ji, ya ji!"

Image

Wannan labari ya ruɗa almajiran. Sai Yesu ya bayyana, "Irin maganar Allah ce. Hanyar mutum ne da ya ji maganar Allah, amma bai gane ta ba, kuma sai Shaiɗan ya ɗauke mashi ita."

Image

"Ƙasar mai dutsi mutum ne wanda ya ji maganar Allah, kuma ya amince da ita da murna. Amma da tsanani da ƙunci suka sa ya faɗi."

Image

"Kasa mai ƙayoyi mutum ne wanda ya ji maganar Allah, amma da lokaci yake wucewa, taraddadin duniya da jarabar dukiya suka fitar da ƙaunar Allah daga zuciyarsa. Sai koyaswar bata anfana me kome ba."

Image

"Amma ƙasa mai kyau mutum ne wanda ya ji maganar Allah, ya gaskanta, kuma ya bada ƴaƴa."

Labarin LMT daga Matiyu 13:1-8, 18-23; Markus 4:1-8, 13-20; Luka 8:4-15