(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

41. Allah Ya Tada Yesu Daga Mattatu

Image

Bayan da sojoji suka giciye Yesu, shugabannin Yahudawa da ba su ba da gaskiya ba, suka cewa Bilatus, "Maƙaryacin nan Yesu, ya ce zai tashi daga mattatu bayan kwana uku. Ya kamata wani ya tsare kushewar don kada almajiransa su sace jikin, kuma su ce ya tashi daga mattatu."

Image

Bilatus ya ce,"Ɗauki waɗansu sojoji, kuma su tsare kushewar yadda suke iyawa." Sai suka ɗaure wurin bisan dutse a ƙofar kabari, kuma suka sa sojoji tsaro don su tabbata ba wanda zai sace jikin.

Image

Ranar bayan da aka bizne Yesu ran Asabar ce, Yahudawa ba su da izinin zuwa kabari wannan ranar. Sai da asuba bayan ranar Asabar, mata da yawa suka shirya zuwa kabarin Yesu don su sa kayan ƙamshi na jana'iza kan jikinshi.

Image

Ba zato ba tsammani sai aka yi girgizar ƙasa. Wani mala'ika mai haske kamar walƙiya ya ɓullo daga sama. Ya ture dutsen da yake rufe kofar kabari, kuma ya zauna a bisan dutsen. Sojojin da suke tsaron kabarin suka tsorota har suka faɗi a ƙasa kamar mattatu.

Image

Da matan suka iso kabarin, mala'ikan ya ce masu, "Kada ku ji tsoro. Yesu ba ya nan.Ya tashi daga mattatu kamar yadda ya faɗa zai yi! Ku duba kabarin ku gani." Matan suka duba cikin kabarin suka ga inda jikin Yesu ya kwanta. Jikin ba ya nan!

Image

Mala'ikan ya cewa matan,"Ku je ku faɗawa almajiran, 'Yesu ya tashi daga mattatu, kuma zai je Galili gaba da ku."

Image

Matan suka cika da tsoro da kuma babbar murna. Sai suka yi gudu suka faɗawa almajiran labari mai daɗi.

Image

Sa'ad da matan suke tafiya domin su ba almajiran labarin mai daɗi, Yesu ya bayyana garesu, kuma sai suka yi masa sujada. Yesu ya ce, "Kadda ku ji tsoro. Ku je ku faɗa wa almajiraina su tafi Galili. Can za su ganni."

Labarin LMT daga Matiyu 27:62-28:15; Marƙus 16:1-11; Luka 24:1-12; Yahaya 20:1-18