(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

3. Ambaliya

Image

Bayan kwanaki da yawa, mutane suka yawaita a cikin duniya. Sai suka zama masu mugunta da yawa. Sun tsananta da yin mugunta har Allah ya yi ƙudurin ya hallaka dukan duniya da ambaliyar ruwa.

Image

Amma Nuhu ya sami tagomashi ga Ubangiji. Mutum ne mai adalci cikin mugayen mutane. Allah ya yi wa Nuhu zancen ambaliyar ruwa da zai abko a duniya. Ya cewa Nuhu ya gina babban jirgin ruwa.

Image

Allah ya cewa Nuhu ya sassaƙa jirgin ruwa mai tsawon meta 140, fadinsa meta 23, tsayinsa meta 13.5. Nuhu, zai yi shi da itace hawa uku, ɗakuna da yawa, soro, da taga. Jirgin zai ɗauki Nuhu, iyalinsa, da dukan irin dabba mai rai lokacin ambaliyar ruwan.

Image

Nuhu ya yi biyayya ga Allah. Shi da ƴaƴansa uku suka gina jirgin kamar yadda Allah ya faɗa masu. Ya ɗauki shekaru da dama don gina jirgin domin yana da girma sosai. Nuhu ya faɗakar da mutane a kan ambaliyar ruwa da za ta zo, ya kuma ambace su, su juyo wurin Ubangiji, amma ba su yarda su gaskanta da shi ba.

Image

Allah ya kuma faɗakar da Nuhu da iyalinsa su tattara abinci isasshe domin kansu da domin dabbobin. Da komi ya shiryu, Allah ya cewa Nuhu lokaci yayi, matarsa, ƴaƴansa uku, da kuma matansu, su shiga cikin jirgin ruwa–mutane takwas ke nan.

Image

Allah ya aika namiji da ta mace daga kowane dabba da tsuntsaye wurin Nuhu don su shiga jirgin su tsira. Allah ya aike iri bakwai maza da iri bakwai mata na kowane dabba da ake iya miƙawa hadaya. Da suka shiga duka cikin jirgin, sai Allah da kansa ya rufe ƙofar.

Image

Sai aka yi ta kwararo ruwa bisa duniya. Aka yi ruwa kwana arba'in da dare arba'in ba fasawa! Ruwa kuma ya ɓulɓulo hallo daga ƙasa. Ruwa ya mamaye dukan duniya har manyan tuddai sun ciyu.

Image

Dukan masu rai cikin ƙasa suka mutu, banda mutanen da dabbobbin da suke cikin jirgin. Jirgin yana yawo kan ruwaye, yana ƙumshe da duk abin da cikinsa da suka tsira.

Image

Bayen da ruwa ya tsaya, jirgin ya yi yawo kan ruwaye wata biyar, kuma a lokacin nan ruwayen suka fara janyewa. Sai wata rana jirgin ya kafe kan babban tudu, amma duniya a rufe take da ruwa. Bayan wata uku tsinin tuddai ya fara ganuwa.

Image

Bayan kwana arba'in kuma, Nuhu ya saki tsuntsun ake kira hankaka ya gani in ruwan ya janye daga ƙasa. Hankakan ya yi ta kai da kawowa neman busasshiyar ƙasa amma bi samu ba.

Image

Bayan kwanaki Nuhu ya aike da tsuntsu ma sunan kurciya, amma ita ma ba ta samu busasshiyar ƙasa ba, sai ta dawo wajen Nuhu. Bayan wani sati ya sake aikin kurciyar, sai ta dawo da ganyen zaitun a bakinta! Ruwa ya rage, kuma itatuwa sun sake tsirowa!

Image

Nuhu ya ƙara jira wani sati, ya kuma aike da kurciyar gami na uku. Wannan lokaci sai ta samu wurin zama, ba ta ƙara komowa ba. Ruwayen suka ci gaba da janyewa!

Image

Da wata biyu suka wuce, sai Allah ya cewa Nuhu, "Kai da iyalinka, da dukan dabbobin ku fita daga jirgin ruwa yanzu. Ku hayayyafa ku yi ƴaƴa da jikoki ku kuma cika duniya." Sai Nuhu da iyalinsa suka fito daga jirgin ruwa.

Image

Bayan da Nuhu ya fita daga jirgin ruwa, sai ya gina bagadi ya miƙa hadaya na duk irin dabba da ake iya miƙawa. Allah kuwa ya ji daɗin hadayar, sai ya albarkaci Nuhu da iyalinsa.

Image

Allah ya ce, "Na yi alkawali ba zan ƙara la'antar ƙasa ba domin zunuben mutane, ko in hallaka duniya da ambaliyar ruwa, ko da shi ke mutane suna ɗauke da zunubi tun lokacin yarantakarsu.

Image

Allah ya kafa bakangizo wato shaidar alkawarinsa. Duk lokacin da bakangizon ya fito a sama, Allah yana tunawa da alkawarin da ya yi haka nan mutane ma.

Labarin LMT daga Farawa 6-8