(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

21. Allah Ya Ƙadara Aiko Almasihu

Image

Tun da farko, Allah ya nufi ya aiko da Almasihu. Alkawali na fari na zuawan Almasihu ya zo ga Adamu da Hawa'u. Allah ya yi alkawalin cewa da wani daga zuriyar Hawa'u za a haife shi, zai kuje kan maciji. Macijin da ya yaudari Hawa'u Shaitan ne. Alkawalin yana nufin Almasihu zai ci nasara da Shaitan cikaka.

Image

Allah ya yi wa Ibrahim alkawali cewa ta wurin shi dukan al'ummai na duniya za su sami albarka. Wannan albarka za ta samu cika lokacin da Almasihu zai zo cikin zamani mai zuwa. Zai zama hanyar mutanen dukan duniya su samu ceto.

Image

Allah ya yi wa Musa alkawali da a zamani mai zuwa, zai tado da wani annabi kamar Musa. Wanga wani alkawali ne a kan Almasihu da zai zo bayan ɗan lokaci.

Image

Allah ya yi wa Dauda alkawali ɗaya daga zuriyarsa zai yi mulkin mutanensa har abada. Ke nan yana nufin Almasihu zai zama ɗaya daga zuriyar Dauda ta jiki.

Image

Ta wurin annabi Irmiya, Allah ya faɗa cewa zai yi Sabon Alkawali, amma ba kamar alkawalin da Allah ya yi ba da Isra'ila a Sinai. Cikin Sabon Alkawalin, Allah zai rubuta dokarsa cikin zuciyar mutane, mutane za su san Allah da kansu, za su zama mutanensa, kuma Allah zai gafarta zunubainsu. Almasihu zai fara Sabon Alkawali.

Image

Annabawan Allah kuma suka ce Almasihu zai zama annabi, firist da kuma sarki. Annabi mutum ne mai jin maganar Allah, kuma yana furta maganar Allah ga mutane. Almasihun da Allah ya alkawarta ya aiko zai zama cikakken annabi.

Image

Firistocin Isra'ilawa suka miƙa hadayu ga Allah da sunan mutane a maimakon horon don zunubainsu. Firistoci kuma suka yi addu'a ga Allah domin mutane. Almasihu zai zama cikakken babban firist da zai bada kan shi sadaka, kyaukyawar hadaya ga Allah.

Image

Sarki mutum ne mai mulki bisan daula, kuma yana shar'anta mutane. Almasihu zai zama cikakken sarki da zai zauna a gadon sarauta na kakan shi Dauda. Zai yi mulki bisan dukan duniya har abada, kuma zai yi shari'a da gaske, kuma ya ɗauki shawarorin da suke daidai.

Image

Annabawan Allah sun yi annabcin wasu abubuwa da yawa a kan Almasihu. Annabi Malakai ya bada labari cewa da wani babban annabi zai zo kamin Almasihu ya iso. Annabi Ishaya ya yi annabci cewa da Almasihu, za a haife shi ta wurin budurwa. Annabi Mika ya ce da za a haife shi a cikin garin Baitalami.

Image

Annabi Ishaya ya faɗa cewa Almasihu zai rayu a Galili, ya ƙarfafa mutanen da zuciyarsu ta karye, ya furta saki ga ɗauraru da kuma na cikin kaso. Ya kuma yi annabci cewa da Almasihu zai warkar da marassa lafiya da kuma kurame, makafi, baibai ko guragu.

Image

Annabi Ishaya hallo ya yi annabci cewa Almasihu zai zama abin ƙyama, kuma za a yas da shi ba tare da ya yi wani abu ba. Waɗansu annabawa sun faɗa cewa da waɗanda suka kashe Almasihu za su jefa kuri'a a kan kayan jikinshi, kuma ɗaya daga abokansa zai ci amanarsa. Annabi Zakariya ya yi annabci cewa abokin za a biya shi kuɗi talatin na azurfa na cin amanar Almasihu.

Image

Annabawan kuma suka faɗi yadda Almasihu zai mutu. Ishaya ya yi annabci da mutane za su tofa masa yau, su yi masa ba'a, kuma su duke Almasihu. Za su soke shi kuma zai mutu cikin azaba mai zafi da raɗaɗi. Ko da yake bai yi kome ba.

Image

Annabawa suka ƙara cewa da Almasihu zai zama cikakke, maras zunubi. Zai mutum don ya ɗauki horo saboda zunubin sauran mutane. Horon shi zai kawo salama tsakanin Allah da mutane. Sabili da wannan, nufin Allah ne ya murƙushe Almasihu.

Image

Annabawa sun riga faɗa cewa da Almasihu zai mutu, kuma Allah zai tashe shi daga matattu. Ta wurin mutuwa da tashin Almasihu, Allah zai cika tsarinsa na ceton masu zunubi, kuma ya fara Sabon Alkawali.

Image

Allah ya bayyana wa annabawa abubuwa da yawa a kan Amasihu, amma Almasihun ba ya zo ba a lokacin ko ɗaya daga wannan annabawan. Hiye da shekaru 400 bayan annabci na ƙarshe, a lokaci daidai Allah zai aiko da Almasihu cikin duniya.

_Labarin LMT daga : Farawa 3:15; 12:1-3; Kuɓowar Shari'a 18:15; 2 Sama'ila 7; Irmiya 31; Ishaya 59:16; Daniel 7; Malaci 4:5; Ishaya 7:14; Mika 5:2; Ishaya 9:1-7; 35:3-5; 61; 53; Zabura 22:18; 35:19; 69:4; 41:9; Zakariya 11:12-13; Ishaya 50:6; Zabura 16:10-11 _