(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

42. Yesu Ya Koma Sama

Image

A ranar da Yesu ya tashi daga mattatu, biyu daga almajiransa suna tafiya wani gari a kusa. Sa'ad da suke tafiya, sun a zancen abin da ya faru ga Yesu. Sun yi zato cewa da shi ne Almasihu, amma sai aka kashe shi. Yanzu matan suka ce yana da rai kuma. Ba su san wanda za su gaskanta ba.

Image

Yesu ya kusato da su, kuma ya fara tafiya tare da su, amma ba su gane shi ba. Ya yi tambaya zance me suke yi, sai suka faɗa masa dukan abin ban mamaki ba ya faru da Yesu kwanakin da suka wuce. Sun yi tsammani suna magana da wani baƙo da bai san abin da ya faru ba a Urshalima.

Image

Sai Yesu ya fasarta masu abin da maganar Allah ta ce a kan Almasihu. Ya tuna masu cewa da annabawa sun riga sun faɗi Almasihu zai sha wahala, kuma za a kashe shi, amma zai kuwa tashi a kwana na uku. Da suka iso garin inda mutanen biyu suka nufa su zauna, dare ya kusa yi.

Image

Mutanen biyu suka gayaci Yesu ya zauna tare da su, sai ya yarda. Sa'ad da suka yi shirin ci abincin dare, Yesu ya ɗauki guntun gurasa, ya yi godiya ga Allah, kuma ya karya ta. Nan da nan sai suka gane shi ne Yesu. Amma a wannan lokacin, sai ya bace daga gabansu.

Image

Mutanen biyu suka ce a tsakaninsu, "Yesu ne! Shi ya sa zukatanmu suka huru lokacin da ya fasarta mana maganar Allah! Nan take sai suka koma Urshalima. Da suka iso, suka fadawa almajiran, "Yesu yana da rai! Mun gane shi!"

Image

Yayin da almajiran suke hira, Yesu, ba zato ba tsammani, ya bayyana garesu cikin ɗakin ya ce, "Salama a gareku!" Almajiran sun yi tsammani fatalwa ce, amma Yesu ya ce,"Me ya sa ku ke tsoro, kuma kuna shakka? Ku dubi hannuwa na da ƙafafuwa na. Fatalwu ba su da jiki kamar yadda nake da." Domin su tabbata shi ba fatalwa ba ne, sai ya tambaye su abinci. Suka ba shi ɗan guntun kifi a dafe, kuma ya ci shi.

Image

Yesu ya ce, "Na riga na gaya maku cewa da duk abin da aka rubuta a kaina cikin maganar Allah sai ya cika." Sai ya buɗe hankalinsu don su gane maganar Allah. Ya ce, "A rubuce yake da daɗewa cewa Almasihu zai sha wahala, ya mutu, kuma ya tashi daga mattatu a kwana na uku."

Image

"A rubuce yake kuma cikin littafin addini cewa da almajirai za su shaidawa kowa ya tuba domin ya samu gafarar zunubainsa. Za su yi haka farawa cikin Urshalima, kuma za su je wurin dukan mutane ko'ina. Ku ne shaiduna na dukan waɗannan abubuwan."

Image

Cikin kwanaki arba'in bayan tashinsa, Yesu ya bayyana ga almajiransa sau da yawa. Wata rana ya bayyana ga mutane hiye da 500 gami guda! Ya tabbatarwa almajiransa ta hanyoyi da dama yana da rai, kuma ya koyas da su a kan mulkin Allah.

Image

Yesu ya cewa almajiransa,"An ba ni dukan iko cikin sama da cikin ƙasa. Sai ku je ku almajirtar da dukan ɗarikun mutane, kuna yi masu baftisma cikin suna Uba, da ɗa, da Ruhu Mai Tsarki, kuma ku koyas da su, su yi biyayya da duk abin da na umurce ku. Ku tuna ina tare da ku kullum."

Image

Kwana arba'in bayan da Yesu ya tashi daga mattatu, ya fadawa almajiransa, "Ku zauna a Urshalima har sa'ad da Ubana ya ba ku iko randa Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku." Sai Yesu ya hau sama, kuma gajimare ya ɓoye shi daga idanunsu. Yesu ya zauna a hannun damar Allah don ya yi mulki bisan dukan komi.

Labarin LMT daga Matiyu 28:16-20; Marƙus 16:12-20; Luka 24:13-53; Yahaya 20:19-23; Ayukan Manzani 1:1-11