(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

19. Annabawa

Image

A cikin dukan tarihin Isra'ilawa, Allah ya aike masu da annabawa. Annabawan sun ji saƙonni daga Allah, sun kuma faɗawa mutane saƙonni na Allah.

Image

Iliya ne annabi a lokacin da Ahab yake mulki kan Isra'ila. Ahab mugun mutum ne da ya tura mutane su bauta wa gumki mai suna Ba'al. Iliya ya cewa Ahab, "Ba za ayi ruwa ko raɓa ba a cikin mulkin Isra'ila har na yi magana." Wannan ya husatar da Ahab.

Image

Allah ya ambaci Iliya ya je kusan wani rafi, ya ɓoye wa Ahab da ya nema ya kashe shi. Kowace safiya da kowane dare, tsuntsaye suke kawo masa gurasa da nama. Ahab da rundunar sojojinsa suka nemi Iliya, amma ba su iya samunsa ba. Farin ya yi tsanani sosai har rafin ruwan ya bushe.

Image

Sai Iliya ya tafi wata maƙobciyar ƙasa. Wata mace da mijinta ya mutu da ɗanta a wannan ƙasar, abincinsu ya kusa ƙarewa saboda fari. Amma sun kula da Iliya, kuma Allah ya tanada dominsu har garin abinci da mai ba su ƙare ba. Kamar haka suna da abinci lokacin yunwa. Iliya ya zauna tare da su shekaru da yawa.

Image

Bayan shekara uku da rabi, Allah ya cewa Iliya ya koma mulkin Isra'ila, ya yi magana da Ahab domin zai aiko da ruwan sama kuma. Da Ahab ya sake ganin Iliya, sai ya ce, "Kai ne mafarin wahalarmu!" Iliya ya amsa ya ce, "Kai ne ka janyo matsalar! Tunda ka bar Yaweh, Allah na gaskiya, kuma ka bauta wa Ba'al. Kawo dukan mutanen mulkin Isra'ila bisan dutsen Karmel."

Image

Dukan mutanen mulkin Isra'ila, da annabawan Ba'al 450, suka zo dutsen Karmel. Iliya ya cewa mutanen, "Har yaushe za ku taurare tunaninku? In Yahweh ne Allah, ku bauta masa! In Ba'al ne allah, ku bauta masa!"

Image

Sai Iliya ya cewa annabawan Ba'al, "Ku kashe bijimi, ku shirya shi domin hadaya, amma kadda ku kunna wuta. Zan yi haka nan. Allahn da ya amsa da wuta shi ne Allah na gaskiya." Sai firistocin Ba'al suka shirya hadayar amma ba su kunna wutar ba.

Image

Sai annabawan Ba'al suka yi addu'a ga Ba'al, "Ka saurare mu Ba'al! Dukan rana suka yi addu'a, kuma suka yi ƙara har suka yanke jikinsu da wuƙaƙe, amma babu amsa.

Image

A ƙarshen yini, Iliya ya shirya hadaya ga Allah. Sai ya cewa mutane su zuba ruwan tulu goma sha biyu bisan bagadin har yayin da naman, da icen, kuma da ƙasa kewaye da bagadin suka jiƙa sarai.

Image

Sai Iliya ya yi addu'a, "Yahweh, Allah na Ibrahim, da Ishaƙu, da Yakubu, gwada mana yau kai ne Allah na Isra'ila, kuma ni bawanka ne. Ka amsa mani domin mutane su sani kai ne Allah na gaskiya."

Image

Nan da nan sai wuta ta sauko daga sama, ta cinye nama, da ice, da duwatsu, da ƙasa, har da ruwan kewaye da bagadin. Da mutane suka ga haka, sai suka rusuna ƙasa suka ce, "Yahweh ne Allah! Yahweh ne Allah!"

Image

Sai Iliya ya ce, "Kada ku bar ko ɗaya daga annabawan Ba'al su tsira!" Sai mutanen suka kama annabawan Ba'al, suka kai su wani wuri can suka kashe su.

Image

Sai Iliya ya cewa sarki Ahab, "Koma maza-maza cikin birnin, domin ruwan sama yana zuwa." Nan da nan sai samaniya ta yi baƙi, kuma babban ruwa ya fara. Yahweh ya gama yin fari, kuma ya nuna shi ne Allah na gaskiya.

Image

Bayan lokacin Iliya, Allah ya zaɓi wani mutum mai sunan Elisha ya zama annabinsa. Allah ya yi al'ajabai da yawa ta wurin Elisha. Ɗaya daga al'ajabin ya faru ga Na'aman, wani shugaba abokin gaba, da ya ke da kuturta. Ya ji labarin Elisha, sai ya je ya roƙi Elisha ya warkasda shi. Elisha ya faɗawa Na'aman ya yi wanka sau bakwai cikin kogin Urdun.

Image

Da fari Na'aman ya husata, kuma ba ya yi biyayya ba domin ba kangado. Amma bayan wani lokaci, ya canza tunaninsa, ya je ya tsoma kansa sau bakwai cikin kogin Urdun. Da ya fito daga ruwan a kari na ƙarshe, fatar jikinsa ta warke kwatakwata! Allah ya warkar da shi.

Image

Allah ya aike da wasu annabawa da yawa. Su duka sun fadawa mutane su bar bautar gumaka, kuma su nuna adalci da tausayi ga sauran. Annabawan sun faɗɗakar da mutane da, in ba su daina mugunta ba, suka yi biyayya ga Allah, to Allah zai hukunta su kamar masu zunubi.

Image

Yawancin lokaci, mutanen ba su yi biyayya ga Allah ba. Sun wahalta annabawa sau da yawa har wasu wokatai sun kashe su. Wata sa'a, sun jefa annabi Irmiya cikin rijiya busasshiya, kuma suka bar shi ya mutu. Ya kamu cikin laka cikin rijiyar, amma loton nan sai sarkin ya ji tausayin shi, sai ya umurta a janyo shi waje daga cikin rijiya kafin Irmiya ya mutu.

Image

Annabawa sun ci gaba da magana don Allah, ko da yake mutane sun tsane su. Sun fadakar da mutane cewa Allah zai hallaka su in ba su tuba ba. Suka kuma tuna wa mutane alkawali da Allah ya yi na Al'masihu mai zuwa.

Labarin LMT daga: 1 Sarakuna 16-18; 2 Sarakuna 5; Irmiya 38