(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

17. Alkawalin Allah ga Dauda

Image

Saul ne sarki na fari a Isra'ila. Yana da tsawo, kuma kyaukyawa ne, kamar yadda mutanen suke so. Saul ya zama sarki kirki ƴan shekaru na fari. Amma sai ya koma mai mugunta, mai rashin biyayya ga Allah. Sai Allah ya zaɓi wani mutum daban, wanda wata rana zai zama sarki maimakon shi.

Image

Allah ya zaɓi saurayi Bayahude mai sunan Dauda ya zama sarki bayan Saul. Dauda makiyayi ne daga Betalami. A lokaci daban-daban, sa'ad da yake kula da garken ubansa, Dauda ya kashe zaki da beyar (ko "ours"-Fr.) da suka faɗa wa ragunansa. Dauda mai tawali'u ne kuma mai adalci ne, yana tsoron Allah, yana kuma yi masa biyayya.

Image

Dauda ya zama baban shugaban sojoji. Lokacin da Dauda yake saurayi ya yake baban jarumi mai sunan Goliyat. Goliyat, baban jarami horarre mai ƙarfi ƙwarai ne. Yana da tsawon mita uku, amma Allah ya taimake Dauda, ya kashe Goliyat ta haka ya ceci Isra'ilawa. Bayan wannan Dauda ya ci nasara da yawa bisan magabtan Isra'ila, dalilin haka mutane sun yi yabonshi.

Image

Saul ya cika da kishi domin mutane su fi ƙaunar Dauda. Saul ya nema sau da yawa ya kashe shi, sai Dauda ya ɓoye ma Saul. Wata rana, Saul yana neman Dauda don ya kashe shi, Saul ya je cikin kogon dutsen inda Dauda ya boƴe, amma Saul bai gane shi ba. Dauda yana kusa da Saul, yana kuma iya kashe shi amma bai yi ba. Maimakon haka, Dauda ya yanke ƙaɗan daga rigar Saul domin Saul ya sani Dauda ba zai kashe shi ba don ya zama sarki.

Image

Sai wata rana, Saul ya mutu cikin yaƙi, kuma Dauda ya zama sarkin Isra'ila. Sarki ne mai kirki, kuma mutane suna ƙaunarsa. Allah ya albarkace shi, kuma ya ba shi nasara cikin komi. Dauda ya yi yaƙi da yawa, kuma Allah ya taimake shi ya yi nasara da abokan gaban Isra'ila. Dauda ya ci nasara Urushalima sai ya maida ta baban birnin ƙasa. Lokacin mulkin Dauda, Isra'ila ta zama da ƙarfi da arziki.

Image

Dauda ya yi niya ya gina haikali inda dukan Isra'ilawa ke iya sujada ga Allah su kuma miƙa masa hadayu. Shekaru 400 da suka wuce, mutanen suna sujadarsu da hadayu ga Allah cikin alfarwar da Musa ya kafa.

Image

Amma Allah ya aike da annabi Natan wurin Dauda da wannan saƙo: "Domin kai mutumen yaƙi ne, ba za ka gina haikalin ba domina. Ɗanka ne zai gina shi. Amma zan sa maka albarka sarai. Ɗaya daga zuriyarka zai yi mulkin mutanena har abada!" Makaɗaicin zuriyar Dauda wanda ke iya mulki har abada Al'masihu ne." Al'masihu zaɓaɓɓe ne na Allah, shi ne mai ceton mutanen duniya daga zunubensu.

Image

Da Dauda ya ji waɗannan maganganu, sai nan da nan ya yi godiya ya yabi Allah domin ya yi masa wannan babban alkawali da daraja da albarku. Dauda bai sani ba randa Allah zai cika waɗannan abu. Kamar yadda ya faru, Isra'ilawa sai sun yi jira lokaci mai tsawo kafin Al'masihu ya zo, kusan shekara 1000.

Image

Dauda ya yi mulki da adalci da bangaskiya shekaru da yawa, kuma Allah ya albarkace shi. Duk da wannan, kusan ƙarshen rayuwarshi, ya yi wa Allah babban zunubi.

Image

Wata rana, sa'ad da dukan sojojin Dauda suke da nesa cikin yaƙi, ya leƙa daga gidansa, sai ya ga mace kyaukyawa tana wanka. Sunanta Bat-sheba.

Image

Maimakon ya daina, Dauda ya aiki wani ya kawo mashi ita. Ya kwana da ita, kuma ya aika ta gida. Bayan ɗan lokaci kaɗan Bat-sheba ta yi wa Dauda saƙo cewa tana da juna biyu.

Image

Mijin Bat-Sheba, sunansa Uriya, ɗaya ne daga cikin sojojin Dauda mafi ƙwari. Dauda ya kira Uriya ya komo daga yaƙi, kuma faɗa masa ya je wajen matarsa. Amma Uriya ya ƙi ya koma gida ya bar sauran sojoji cikin yaƙi. Sai Dauda ya aike Uriya ya koma cikin yaƙi, kuma ya umurci shugaban ya sa shi a gaba inda akwai tsanani don a kashe shi.

Image

Bayan da aka kashe Uriya, Dauda ya auri Bat-Sheba. Da jimawa, sai ta haifi ɗa. Allah ya husata sarai da abin da Dauda ya aikata, sai ya aike da annabi Natan ya faɗawa Dauda ƙazamin zunubinshi. Dauda ya tuba daga zunubin shi, kuma Allah ya gafarta masa. Sauran kwanakinsa, Dauda ya bi, ya kuma yi biyayya ga Allah har a cikin lokacin wahala.

Image

Amma hukuncin zunubin Dauda shi ne ɗansa namiji ya rasu. Akwai kuma jayayya cikin iyalin Dauda duka sauran rayuwarshi. Ikon Dauda ya kuma rage ƙwarai. Ko da yake Dauda ya kasa wani lokaci, Allah bai janye alkawalinsa ba. Bayan wani lokaci, Dauda da Bat-Sheba sun haifi wani yaro, sun kuma kira shi Sulemanu.

Labarin LMT daga : 1 Sama'ila 10; 15-19; 24; 31; 2 Sama'ila 5; 7; 11-12