(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

32. Yesu Ya Warkas da Mutum Mai Aljan, Kuma da Mace Maras Lafiya

Image

Wata rana, Yesu da almajiransa suka shiga jirgin ruwa suka tsallaka tafki zuwa wata ƙasa inda Garasinawa suke.

Image

Da suka kai wancan gefen tafkin, wani mutum mai aljannu ya zo da gudu wurin Yesu.

Image

Wannan mutum yana da ƙarfi sosai har da ba wanda ya iya riƙe shi. Mutane har sun ɗaure hannuwansa da ƙafafuwansa da igiyoyin ƙarfe, amma ya ci gaba da karyasu.

Image

Mutumen ya zaune a bakin kushewu. Wannan mutum ya kan yi ƙara dukan rana da dukan dare. Ba shi da sutura, kuma yana ta yanke kanshi da duwatsu.

Image

Da mutumen ya zo wurin Yesu, ya faɗi a gwiwowinsa a gaban shi. Yesu ya cewa aljannin, "Fito daga mutumen nan!"

Image

Mutumen mai aljannin ya yi ƙara da murya mai ƙarfi, "Me kake so da ni Yesu, Ɗan Allah Maɗaukaki? Don Allah kar ka wahalshe ni!" Sai Yesu ya tambayi aljannin, "Mene sunanka?" Ya amsa, "Sunana Dubu, domin mu da yawa ne." (Dubu ƙangin dubu da dubunnai sojojin Ramawa ne).

Image

Aljannun suka roƙi Yesu, "Don Allah kada ka kore mu nesa da nan!" Akwai garken aladu suna kiwo a kusan wurin. Sai aljannun suka riƙi Yesu, "Don Allah aika mu cikin aladun kanbacin!" Yesu ya ce, "Ku tafi!"

Image

Aljannun suka fita daga mutumen, kuma suka shiga aladun. Aladun suka gudu ta gangara cikin tafkin suka nutse. Akwai kusan aladu 2,000 cikin garken.

Image

Da makiyayan aladun suka ga abin da ya faru, sun yi gudu cikin gari, kuma suka shaidawa kowa da sun sadu da Yesu da abin da ya yi. Mutanen garin suka zo suka ga mutumen mai aljannun yana zaune hankali kwance, yana saye da kayan jiki, kuma ya zama mutum mai hankali.

Image

Mutanen sun tsorota, kuma suka ambaci Yesu ya bar garin. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa, kuma ya yi shirin tafiya. Mutumen mai aljannun a da, ya roƙi Yesu ya raƙa shi.

Image

Amma Yesu ya ce masa, "A'a, so nake ka je gida ka shaidawa abokai da iyalinka abin da Allah ya yi maka, kuma ta ƙaƙa ya ji tausayinka."

Image

Sai mutumen ya tafi, kuma ya shaidawa kowa abin da Yesu ya yi masa. Dukan wanda ya ji labarin ya cika da mamaki da murna.

Image

Yesu ya koma wancan gefen tafkin. Bayan da ya isa can, taro mai yawa ya kewaye shi ya matse shi kusa-kusa. Cikin taron akwai wata mace da take fama da ciwon zubda jini har tsawon shekara goma sha biyu. Ta kashe dukan kuɗinta wurin likitoci don su warkas da ita, amma sai ta ƙara lalacewa.

Image

Ta ji labari Yesu ya warkas da marasa lafiya da yawa, kuma ta yi tunani, "Na tabbata in na iya taɓa kayan jikin Yesu kaɗai ma, ina iya warkewa ni ma!" Sai ta matso kusa da bayan Yesu, kuma ta taɓa kayanshi. Da ta taɓa su, sai jinin ya tsaya!

Image

Nan da nan, Yesu ya ji a jikinshi da wani iko ya fita daga gareshi. Sai ya juya, kuma ya tambaya, "Wa ya taɓa ni?" Almajiran suka amsa masa, "Akwai mutane da yawa kewaye da kai, kuma suna faɗa maka. Ƙaƙa za ka tambaya, 'Wa ya taɓa ni?'

Image

Macen ta faɗin a gabansa a gwiwawunta, tana rawar jiki, kuma ta tsorota. Sai ta gaya masa abin da ta yi, kuma ta sami lafiya. Yesu ya ce mata, "Bangaskiyarki ta warkasda ke. Je ki cikin salama."

Labarin LMT daga Matiyu 8:28-34; 9:20-22; Marƙus 5:1-20; 5: 24b-34; Luka 8:26-39; 8:42b-48

~~COMPLEX_TABLES~~