(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

27. Labarin Basamariye Mai Jinƙai

Image

Wata rana, wani babban masanin shari'ar Yahudawa ya zo wurin Yesu domin ya gwada shi. Sai ya ce, "Malam, me zan yi in gadi rai na har abada?" Yesu ya amsa, "Me aka rubuta cikin shari'ar Allah?"

Image

Masanin shari'ar ya amsa masa cewa, shari'ar Allah ta ce, "Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da ƙarfinka, kuma da tunaninka. Kuma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka." Yesu ya amsa masa cewa, "Haka ne! Yi haka, kuma za ka rayu."

Image

Amma Bafarisen yana so ya gwada shi yana daidai, sai ya yi tambaya, "Wane ne maƙwabcina?"

Image

Yesu ya amsawa Bafarisen ta wurin gaya mashi wani labari, "Akwai wani Bayahude da ya tafi balaguro daga Urshalima zuwa Yeriko."

Image

"Lokacin da mutumen yake tafiya, sai ƴan fashi suka faɗa shi. Suka sace dukan abin da yake da, kuma suka duke shi har ya kai bakin mutuwa, Sa'annan suka tsere."

Image

"Lokaci kaɗan bayan wannan, wani firist Bayahude ya biyo hanyar. Da wannan shugaban addinin ya ga mutumen da aka yi wa sata, kuma aka yi masa duka, ya ya koma wata hanya, ya manta da shi mutumen da yake bukatar taimako, kuma ya yi tafiya tasa."

Image

"Ba da daɗewa ba, wani Balawiye ya zo kan hanyar. (Lawiyawa kabila ce ta Yahudawa da suke taimakon firistoci a Haikali). Balawiyen shi ma ya sauya hanya, ya manta da mutumen da aka yi wa sata, kuma aka yi masa duka."

Image

"Mutumen mai zuwa kan hanyar Basamariye ne. (Samariyawa wata zuriyar Yahudawa ne da suka auri mutanen wasu kabila. Samariyawa da Yahudawa ba sa ƙaunar juna). Amma da Basamariyen ya ga Bayahude a kwance, sai ya yi juyayinshi ƙware. Sai ya lura da shi, kuma ya ɗaure ciyonsa."

Image

"Basamariyen ya ɗaura mutumen kan jakinshi, kuma ya kai shi wani gida a shashen hanyar, inda ya kula da shi."

Image

"Washe gari, Basamariyen yana bukata ya ci gaba da bulaguronsa. Ya bada ƴan kuɗi ga mutumen da ke kula da gidan baƙin, kuma ya ce, "Ka kula da shi, kuma in ka kashe kuɗi fiye da haka, zan biya ka in na dawo."

Image

Sai Yesu ya tambayi Bafarisen, "Me kake tunani? Wanne ne daga cikin mutanen uku maƙwabcin mutumen da aka yi wa sata, kuma aka yi wa duka?" Ya amsa masa, "Wanda ya ji tausayinsa." Yesu ya ce masa, "Je ka, ka yi haka nan."

Labarin LMT daga Luka 10: 25-37