(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

44. Bitrus da Yahaya Sun Warkas da Almajiri

Image

Wata rana, Bitrus da Yahaya suka tafi Haikali. Da suka kusato ƙofar Haikalin, sai suka ga wani gurgu yana barar kuɗi.

Image

Bitrus ya dubi gurɓatacen mutumen ya ce, "Ba ni da kuɗin da zan baka. Amma zan baka abin da na ke da. A cikin sunan Yesu, tashi kuma ka yi tafiya!"

Image

Nan da nan Allah ya warkas da gurɓatacen mutumen, kuma ya fara tafiya, yana tsalle ko'ina, ya kuwa yabi Allah. Mutanen cikin filin Haikalin suka yi mamaki.

Image

Taron jama'a suka zo da sauri su ga mutumen da ya warke. Bitrus ya ce masu, "Me ya sa ku ka yi mamaki da wannan mutum ya warke? Ba mu warkas da shi ba ta wurin ikon kanmu ko kirkinmu. Amma, ikon Yesu da bangaskiyar da Yesu ya bayas ta warkas da mutumen,"

Image

"Ku ne wanda ya faɗawa gwamnatin Roma ya kashe Yesu. Ku kashe mafarin rai, amma Allah ya tashe shi daga mattatu. Ko da yake ba ku gane abin da ku ke cikin yi ba, Allah ya yi anfani da ayyukanku ya cika annabci da ya ce Almasihu zai sha wuya, kuma ya mutu. Yanzu, tuba kuma ku juya ga Allah domin a wanke zunubainku.

Image

Shugabannin Haikalin suka damu ƙware da abin da Bitrus da Yahaya suke cewa. Sai suka kama su, suka jefa su cikin kurkuku. Amma da yawa daga mutanen suka gaskanta da saƙon Bitrus, kuma yawan mutane da suka bada gaskiya ga Yesu ya ƙaru har ya kai kusan 5,000.

Image

Ranar gobe, shugabannin Yahudawa suka kai Bitrus da Yahaya wurin babban firist da sauran shugabannin addinai. Suka tambayi Bitrus da Yahaya,"Da wane iko ku ka warkar da gurɓatacen mutumen?"

Image

Bitrus ya amsa masu,"Wannan mutum ya tsaya kafin ku warkas ta wurin ikon Yesu Almasihu. Kun giciye Yesu, amma Allah ya tashe shi zuwa rai kuma! Kun yashe shi, amma babu wata hanya ta samun ceto in ba ta wurin ikon Yesu ba!"

Image

Shugabannin suka damu da yadda Bitrus da Yahaya suka yi magana a fili, gama suka iya gani waɗannan mutane ba su yi nisa cikin sanin ilimi ba. Amma sai suka tuna da su mutane sun yi tafiya tare da Yesu. Bayan da sun razana Bitrus da Yahaya, sai suka bar su, suka tafi.

Labarin LMT daga Ayyukan Manzanni 3: 1-4:22