(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

13. Alkawalin Allah ga Isra'ila

Image

Bayan da Allah ya bida Isra'ilawa ta cikin Bahar Maliya, ya bida su cikin jeji zuwa dutsen Sinai. A wannan wurin ne Musa ya ga al'amudi mai cin wuta. Mutanen suka yi zango a ƙasan dutsen.

Image

Allah ya cewa Musa da mutanen Isra'ila, "In kun yi mini biyayya, kun kuma riƙe alkawarina, za ku zama nawa masu tamani, mulkin firistoci, al'umma mai tsarki."

Image

Bayan kwana uku, bayan da mutane suka shirya kansu cikin ruhaniya, Allah ya sauko bisa dutsen Sinai da tsawa, da walƙiya, da hayaƙi, da kakaki may babban ƙara. Musa ƙaɗai ne aka yardar ma ya je saman dutsen.

Image

Sai Allah ya basu alkawali, "Ni ne Yahweh, Allahnku, da ya cece ku daga bauta a Masar, Kar ku bautawa waɗansu alloli."

Image

"Kada ku yi kumaka, kada ku bauta masu, domin Ni ne Yahweh, Ina da kishi. Kada ku yi anfani da sunana a banza. Ku kiyaye ranar Asabar da tsarki. Ke nan ku yi dukan aikinku a kwana shida, kwana na bakwai ranar hutu ce da tunawa da Ni.

Image

"Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka. Kada ka yi kisan kai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi ƙarya. Kada ka yi fasiƙanci da matar maƙobcinka ko ka yi ƙyashin gidansa ko kayansa.

Image

Sai Allah ya rubuta wannan dokoki goma bisan alloli biyu na dutse ya kuma baiwa Musa. Allah ya kuma bada waɗansu dokoki kamar haka. Idan mutane sun yi biyayya da dokokin, Allah ya yi alkawalin sa masu albarka da kuma kare su. Idan sun ƙi biyayya Allah zai hore su.

Image

Allah ya kuma ba Isra'ilawa umurni yadda za su gina alfarwa. Ana kiranta alfarwa taruwa, tana da ɗaki biyu a rabe. Babban Firist kaɗai yake iya shiga cikin ɗaki bayan labule domin nan ne Allah yake zaune.

Image

Duk wanda ya yi rashin biyayya ga dokokin Allah, sai ya kawo dabba wurin bagadi gaban alfarwa ta taruwa don hadaya. Firist zai yanke dabbar, ya kuma ƙone ta a bisan bagadin. Jinin dabbar da aka miƙa hadaya ya shafe zunubin mutumin a gaban Allah. Allah ya zaɓi ɗan uwan Musa, Haruna, da zuriyarsa su zama firistoci.

Image

Dukan mutane suka yarda su yi biyayya da dokokin da Allah ya basu, su bauta ma Allah kaɗai, su zama keɓaɓɓun matanensa. Amma bayan lokaci ƙaɗan da wannan alkawalin, sai suka yi zunubi.

Image

Kwana da yawa Musa yana kan dutsen Sinai yana magana da Allah. Mutanen sun gaji da jiran shi ya komo, sai suka kawo zinariya wurin Haruna suka tambaye shi ya gina gumki dominsu.

Image

Haruna ya yi gumkin zinariya kamar ɗan maraƙi. Sai mutanen suka fara bauta masa, suna yi masa hadaya! Allah ya husata sai ya yi ƙudurin ya hallaka su. Amma Musa ya yi addu'a saboda su, sai Allah ya ji roƙonshi ya fasa hallaka su.

Image

Da Musa ya sauko daga dutsen ya ga gumkin, ya husata sosai, sai ya fashe allolin waɗanda suke da dokoki goma a rubuce.

Image

Sai Musa ya kwankatse gumki, ya zama gari, ya watsar da garin cikin ruwa, ya kuma sa mutanen suka sha ruwan. Allah ya aike da alloba bisan mutanen, da yawa suka mutu.

Image

Musa ya hau dutsen kuma, ya yi addu'a Allah ya gafartawa mutanen. Allah ya amshi addu'ar, ya huma gafarta masu. Musa ya rubuta dokokin goma a kan sababbin allolin dutse kanbacin karyayyun. Musa ya sauko daga dutsen ɗauke da Dokokin Goma bisa sabin alloli. Sai Allah ya bida Isra'ilawa daga dutsen Sinai zuwa ƙasar alkawali.

Labarin LMT daga Fitowa 19-34