(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

48. Yesu Ne Alkawartaccen Almasihu

Image

Lokacin da Allah ya halici duniya, komi yana da kyau. Babu zunubi. Adamu da Hawa'u suna ƙaunar juna, kuma suna ƙaunar Allah. Babu cuta ko mutuwa. Haka ne Allah ya so duniya ta zama.

Image

Shaiɗan ya yi magana ta bakin maciji cikin gonar don ya cuci Hawa'u. Sai ita da Adamu suka yi ma Allah zunubi. Domin sun yi zunubi, kowa a duniya yana cuta, kuma kowa yana mutuwa.

Image

Domin Adamu da Hawa'u sun yi zunubi, wani abu mummuna ya faru. Sun koma abokan gaba Allah. Sakamakon wannan, kowane mutum tun sa'an nan, an haife shi cikin zunubi, kuma ya zama abokin gaba na Allah. Zumunci tsakanin Allah da mutane ya baci saboda zunubi. Amma Allah yana da shiri ya gyara wannan zumuncin.

Image

Allah ya yi alkawali cewa wani zuriyar Hawa'u zai murƙushe kan Shaiɗan, kuma Shaiɗan zai ƙuje dudugensa. Wannan yana nufi da Shaiɗan zai kashe Almasihu, amma Allah zai tashe shi zuwa rai kuma, sa'an nan Almasihu zai murƙushe ikon Shaiɗan har abada. Shekaru da dama da suka wuce, Allah ya bayyana da Yesu shi ne Almasihu.

Image

Sa'ad da Allah ya hallaka dukan duniya da ruwa, ya tanada jirgin ruwa don ceton mutanen da suka gaskanta da shi. Ta haka nan, kowa ya cancanci hallaka saboda zunubinsa, amma Allah ya tanada Yesu ya ceci duk wanda ya gaskanta da shi.

Image

Shekaru ɗaruruwa baya, firistoci, kulluyomi, suka miƙa hadayu ga Allah domin mutane su gane hukunci da ya cancanta don zunubainsu. Amma waɗannan hadayu ba su iya ɗauke zunubainsu ba. Yesu ne Babban Firist. Dabam da saura firistoci, ya bada kansa hadaya kaɗai wadda take iya ɗauke zunubin dukan mutane cikin duniya. Yesu ne ingantaccen babban firist saboda ya ɗauki hukunci kowane zunubi da kowa ya aikata.

Image

Allah ya faɗawa Ibrahim, "Dukan kabilun mutane za su sami albarka ta wurinka." Yesu zuriyar Ibrahim ne. Dukan kabilun mutane sun albarkatu ta wurinsa, domin duk wanda yana bada gaskiya ga Yesu, ya sami ceto daga zunubi, kuma ya zama zuriyar ruhaniya ta Ibrahim.

Image

Sa'ad da Allah ya faɗa wa Ibrahim ya miƙa ɗansa Ishaƙu hadaya, Allah ya tanada ɗan rago hadaya a maimakon ɗansa Ishaƙu. Mu duka mun cancanci mutuwa saboda zunubainmu! Amma Allah ya tanada Yesu, Ɗan Ragon Allah, hadaya, ya mutu madadinmu.

Image

Lokacin da Allah ya aike da alloba ta ƙarshe a Masar, ya faɗawa kowane iyalin Isra'ila da su kashe ɗan rago maras aibi, kuma su yaɗa jininsa bisan, da gyaffan ƙofa. Sa'ad da Allah ya gani jinin, sai ya wuce gidan, kuma ba ya kashe ɗiyan farin su maza ba. Wannan yanayi ana kiransa Idin Ƙetarewa.

Image

Yesu ne Idin Ƙetarewarmu. Ingantacce ne, kuma maras zunubi, kuma aka kashe shi lokacin Idin Ƙetarewa. Idan kowa ya gaskanta ga Yesu, jinin Yesu ya biya zunubin mutumen, kuma hukuncin Allah zai wuce kansa.

Image

Allah ya yi alkawali da Isra'ilawa, zaɓɓaɓun mutanensa. Amma yanzu, Allah ya yi wani Sabon Alkawali wanda ya dace da kowa. Sabili da wannan Sabon Alkawalin, kowa daga kowace kabila yana iya zama cikin mutanen Allah, ta wurin gaskantawa ga Yesu.

Image

Musa ya zama babban annabin da ya shaida maganar Allah. Amma Yesu ne mafi girma cikin annabawa duka. Shi Allah ne, duk abin da ya yi, ko faɗa, ayyukane da maganganu na Allah. Saboda shi ne ake kiran Yesu Maganar Allah.

Image

Allah ya yi wa Sarki Dauda alkawali cewa ɗaya daga zuriyarsa zai yi mulki kamar sarki bisan mutanen Allah har abada. Domin Yesu Ɗan Allah ne, kuma Almasihu ne, shi ne wannan zuriya ta ainihi ta Dauda, da take iya mulki har abada.

Image

Dauda ya zama sarkin Isra'ila, amma Yesu shi sarkin dukan duniya ne! Zai dawo kuma ya yi mulkin mulkinsa da adalci da salama, har abada.

Labarin LMT daga Farawa 1-3, 6, 14, 22; Fitowa 12, 20; 2 Sama'ila 7; Ibraniyawa 3:1-6, 4:14-5:10, 7:1-8:13, 9:11-10:18; Wahayin Yahaya 21