(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

25. Shaiɗan Ya Jarabci Yesu

Image

Nan da nan, bayan da aka yi wa Yesu baftisma, sai Ruhu Mai Tsarki ya fita da shi waje cikin jeji, inda ya yi azumin kwana arba'in da dare arba'in. Sai Shaiɗan ya zo wurin Yesu domin ya jaraba shi ya sa shi zunubi.

Image

Shaiɗan ya jarabta Yesu ya ce: "In kai Ɗan Allah ne, juya waɗannan duwatsu su zama gurasa don ka ci!"

Image

Yesu ya amsa ya ce: "A rubuce yake a cikin Maganar Allah cewa mutane ba da gurasa ba kaɗai za su rayu, amma da dukan maganar da ta ke fitowa daga bakin Allah!"

Image

Sai Shaiɗan ya hauda Yesu bisan ƙolin Haikali, kuma ya ce: "In kai Ɗan Allah ne, jefa kanka ƙasa gama a rubuce yake: 'Allah zai umurci mala'ikunsa su tare ka don kar kafafunka su bigi dutse.'"

Image

Amma Yesu ya amsa wa Shaiɗan ta wurin ambatar littafin addini (Tsofon Alkawali). Ya ce: "A cikin Maganar Allah, Ya umurci mutanensa, 'Ba za ka gwada Ubangiji Allahnka ba.'"

Image

Shaiɗan ya gwadawa Yesu dukan mulkokin duniya da darajarsu, kuma ya ce: "Zan baka dukan waɗannan idan ka durƙusa ka bauta mani."

Image

Yesu ya amsa ya ce: "Fita daga wurina, Shaiɗan! A cikin Maganar Allah, Ya umurci mutanensa: "Ku yi wa Ubangiji Allahnku kaɗai sujada, kuma Shi kaɗai za ku bauta wa.

Image

Yesu bai yarda ya faɗa cikin jarabobin Shaiɗan ba, sai Shaiɗan ya bar shi. Sai mala'iku suka zo suka yi masa hidima.

Labarin LMT daga Matiyu 4:1-11; Markus 1:12-13; Luka 4:1-13