(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

49. Sabon Alkawali na Allah

Image

Wani mala'ika ya faɗawa budurwa Maryamu da za ta haifi Ɗan Allah. Sai sa'ad da take nan budurwa, ta haifi ɗa, kuma ta, kira sunansa Yesu. Ke nan, Yesu shi Allah ne kuma mutum ne.

Image

Yesu ya yi al'ajabai da yawa da ya gwada shi Allah ne. Ya yi tafiya a kan ruwa, ya tsayadda iskoki, ya warkas da marasa lafiya da yawa, ya fitar da aljannu da dama, ya tada mattatu da rai, kuma ya juyadda gurasa biyar da kifi biyu cikin abinci isashe domin mutane fiye da 5,000.

Image

Yesu ya zama babban malami, kuma ya yi magana da iko saboda shi Ɗan Allah ne. Ya koyas da cewa kuna bukata ku ƙaunaci waɗansu mutane kamar yadda ku ke ƙaunar kanku.

Image

Ya kuma koyas da ku na bukata ku ƙaunaci Allah fiye da komi, har ma da arzikinku.

Image

Yesu ya ce mulkin Allah ya fi kowane abu tamani a duniya. Abu mafi mahimmanci ga kowa, shi ne ya zama cikin mulkin Allah. Shiga mulkin Allah, sai ka samu ceto daga zunubin ka.

Image

Yesu ya yi koyaswa cewa da wasu mutane za su ƙarɓe shi, kuma su tsira, amma waɗansu za su ƙiya. Ya faɗa cewa wasu mutane suna kama da ƙasa mai kyau. Sun karɓi bisharar Yesu, kuma sun sami ceto. Waɗansu mutane kuwa suna kama da ƙasa mai tauri cikin hanya, inda ƙwayar maganar Allah ba ta shiga, kuma ba ta bada girbi ba. Mutanen nan suka yadda saƙon Yesu, kuma ba za su shiga mulkinsa ba.

Image

Yesu ya koyas da Allah yana ƙaunar masu zunubi sosai. Yana so ya gafarta masu, kuma ya maida su ƴaƴansa.

Image

Yesu ya kuma faɗa mana Allah yana ƙyamar zunubi. Sa'ad da Adamu da Hawa'u suka yi zunubi, ya shafi dukan zuriyarsu. Sakamako, kowane mutum mai zunubi ne, kuma a rabe yake da Allah. Ke nan kowa ya zama abokin gaba na Allah.

Image

Amma Allah yana ƙaunar kowa a cikin duniya har ya bada makaɗaicin ɗansa don duk wanda ya gaskanta da Yesu, ba za a hukunta shi ba don zunubainsa, amma zai rayu da Allah har abada.

Image

Saboda zunubinku, ku masu laifi ne, kuma kun cancanci mutuwa. Allah ya kamata ya yi fushi da ku, amma ya zuba fushinsa bisan Yesu a madadin ku. Sa'ad da Yesu ya mutu a kan giciye, ya karɓi hukuncin ku.

Image

Yesu bai taɓa yin zunubi ba, amma ya zaɓa ya ɗauki hukunci, kuma ya mutu kamar ingantacciyar hadaya mai kawas da zunubainku da zunubain kowane mutum cikin duniya. Sabili da Yesu ya bada kansa hadaya, Allah yana iya gafarta kowane zunubi, ko zunubi mai tsanani ne.

Image

Ayyuka masu kyau ba su iya ceton ku. Ba abin da ku ke iyawa don ku sada zumunta da Allah. Yesu kaɗai yake iya wanke zunubainku. Sai kun gaskanta da Yesu shi ne Ɗan Allah, kuma ya mutu bisan giciye a madadin ku, kuma Allah ya tashe shi da rai.

Image

Allah zai ceci duk wanda ya gaskanta da Yesu, kuma ya karɓe shi kamar Malaminshi. Amma ba zai ceci duk wanda ba ya bada gaskiya ba. Babu damuwa ko kai mai arziki ne ko matalauci ne, ko na miji ko mace, tsofo ko yaro, ko inda kake rayuwa. Allah yana ƙaunarku, kuma yana so ku gaskanta da Yesu don ya yi zumunta da ku.

Image

Yesu yana gayatar ku, ku gaskanta da shi, kuma a yi maku baftisma. Ko kun amince Yesu na Almasihu, makaɗaicin Ɗan Allah? Ko kun amince da ku masu zunubi ne, kuma kun cancanci Allah ya hukunta ku? Ko kun yi imani da cewa Yesu ya mutu kan giciye don ya ɗauki zunubainku?

Image

In kun gaskanta da Yesu da kuma abin da ya yi domin ku, ku Krista ne! Allah ya fitar da ku daga mulkin Shaiɗan na duhu, kuma ya sa ku cikin mulkin Allah na haske. Allah ya kawas da tsofuwar hanyar ku ta yin abubuwa, kuma ya ba ku sabuwar hanyar yin abubuwa.

Image

Idan kai Krista ne, Allah ya gafarta maka zunubainka sabili da abin da Yesu ya yi. Yanzu Allah ya ɗauke ka aboki maimakon abokin gaba.

Image

Idan kai abokin Allah ne, kuma bawan Yesu Malami, za ka so ka yi biyayya da koyaswar Yesu. Ko da yake kai Krista ne, za ka samu jarabawa ta zunubi. Amma Allah amintacce ya ce in ka furta zunubainka, zai gafarta maka. Zai baka ƙarfin yaƙi da zunubi.

Image

Allah ya umurce ku, ku yi addu'a, ku koyi maganarsa, ku bauta masa da sauran Krista, kuma ku faɗawa sauran abin da ya yi maku. Dukan waɗannan abubuwan suna taya ku ku ƙarfafa cikin zumunta da shi.

Labarin LMT daga Romawa 3:21-26, 5:1-11; Yahaya 3:16; Marƙus 16:16; Kolosiyawa 1:13-14; 2 Korintiyawa 5:17-21; 1Yahaya 1:5-10