(Hausa) هَوُسَ: Open Bible Stories

Updated ? hours ago # views See on DCS

39. An Kai Yesu Gaban Kotu

Image

Yanzu cikin tsakiyar dare ne. Sojojin suka kai Yesu gidan babban firist domin babban firist kin ya yi masa tambayoyi. Bitrus yana biye da su daga nesa. Da aka sa Yesu cikin gidan, Bitrus ya tsaya a waje, kuma ya gunguma kansa kusan wuta.

Image

Cikin gidan shugabannin Yahudawa suka kai Yesu gaban shari'a. Suka kawo shaidun ƙarya da yawa suka masa shaidar zur. Duk da wannan, bayanainsu ba su zo dai-dai da juna ba, sai shugabannin Yahudawa ba su iya samu shaidar laifinsa ba. Yesu bai ce komi ba.

Image

A ƙarshe, babban firist ya dubi Yesu a idanu, kuma ya ce, "Faɗa mana, kai ne Almasihu, Ɗan Allah mai rai?"

Image

Yesu ya ce,"Ni ne, kuma za ku gani zaune tare da Allah, ina zuwa daga sama." Babban firist ya tsaga tufafinsa cikin baƙin ciki, kuma ya yi ƙara ga sauran shugabannin addini, "Ba ma bukatar wasu shaidu! Kun ji ya ce shi ne Ɗan Allah. Mene ne shari'arku?"

Image

Shugabanin Yahudawa duka suka amsa wa babban firist, "Ya cancanci mutuwa!" Sai suka ɗaure masa idanu, suka tofa masa yau, suka duke shi, kuma suka yi masa ba'a.

Image

Sa'ad da Bitrus yake jira waje da gidan, wata baiwa ta gane shi, kuma ta ce masa, "Kaima kana tare da Yesu!" Bitrus ya yi musun sa. Da jimawa, wata yarinya ta sake faɗin haka nan, kuma Bitrus ya sake yin musun shi. A ƙarshe, mutanen suka ce, "Mun sani da kana tare da Yesu domin yawancin ku kun fito daga Galili."

Image

Sai Bitrus ya yi shelar cewa,"Bari Allah ya la'antani in na san wannan mutumen!" Nan da nan, sai zakara ya yi cara, kuma Yesu ya juya ya kalli Bitrus.

Image

Bitrus ya tafi nesa, kuma ya yi kuka mai zafi. Lokacinan, Yahuda, wanda ya ci amana, ya gani shugabannin Yahudawa sun shar'anta Yesu ya mutu. Yahuda ya cika da baƙin ciki, kuma sai ya tafi ya kashe kanshi.

Image

Washe gari da asuba, shugabannin Yahudawa suka kai Yesu gaban Bilatus, mai mulkin Roma. Sun zata Bilatus zai ɗora masa laifi, kuma ya sa a kashe shi. Bilatus ya tambayi Yesu,"Kai na sarkin Yahudawa?"

Image

Yesu ya amsa, "Haka ku ka faɗa, amma mulkina ba mulkin ƙasa ba ne. Inda haka ne, da barorina sun yi yaƙi domina. Na zo da duniya in faɗi gaskiar Allah. Duk wanda yake ƙaunar gaskiya yana saurare na." Bilatus ya ce, "Mene ne gaskiyarka?"

Image

Bayan da ya yi magana da Yesu, Bilatus ya fita waje wurin taro ya ce, "Ban samu laifin wannan mutum ba." Amma shugabannin Yahudawa da taron suka yi ƙara, "A giciye shi!" Bilatus ya amsa, "Ba shi da laifi." Amma sai suka yi ƙara da ƙarfi. Sai Bilatus ya sake faɗi sau na uku, "Ba shi da laifi!"

Image

Bilatus ya tsorota da taron kar ya fara zanga zanga, sai ya umurci sojojinshi su giciye Yesu. Sojojin Roma suka yi masa bulala, kuma suka sa masa tufa ta sarauta da rawanin ƙayayuwa. Sai suka yi masa ba'a suna cewa, "Kalli, sarkin Yahudawa!"

_Labarin LMT daga Matiyu 26:57-27:26; Markus 14:53-15:15; Luka 22:54-23:25; Yahaya 18:12-19:16 _